Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

1 Sam 9:10-15 Littafi Mai Tsarki (HAU)

10. Sai Saul ya ce wa baransa, “Maganarka daidai ce, zo, mu tafi.” Suka kuwa tafi garin da mutumin Allah yake.

11. Sa'ad da suka haura zuwa garin, suka gamu da waɗansu 'yan mata za su ɗebo ruwa, suka ce musu, “Maigani yana nan?”

12. 'Yan matan suka amsa, suka ce, “I, yana nan, ai, ga shi nan ma a gabanku, ku hanzarta. Shigowarsa ke nan a garin, domin yau mutane za su ba da sadaka a bagade a kan tudu.

13. Da shigarku garin, za ku same shi kafin ya tafi cin abinci a wurin yin sadakar, can kan tudu, gama jama'a ba za su ci ba, sai ya je ya sa albarka a sadakar, sa'an nan waɗanda aka gayyata su ci. Ku haura yanzu, za ku same shi nan da nan.”

14. Suka kuwa haura zuwa cikin garin. Da shigarsu suka ga Sama'ila ya nufo wajen da suke, za shi wurin da ake yin sujadar.

15. Ana gobe Saul zai tafi wurin Sama'ila, Ubangiji ya bayyana wa Sama'ila.

Karanta cikakken babi 1 Sam 9