Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

Luk 24:1-13 Littafi Mai Tsarki (HAU)

1. A ranar farko ta mako kuwa, da asussuba, suka je wurin kabarin da kayan ƙanshi da suka shirya.

2. Sai suka tarar an mirgine dutsen daga kabarin.

3. Suka shiga ciki, amma ba su sami jikin Ubangiji ba.

4. Tun suna cikin damuwa da abin, sai kawai ga waɗansu mutum biyu a tsaye kusa da su, saye da tufafi masu ƙyalƙyali.

5. Don tsoro, matan suka sunkuyar da kansu ƙasa. Mutanen suka ce musu, “Don me kuke neman rayayye a cikin matattu?

6. Ai, ba ya nan, ya tashi. Ku tuna yadda ya gaya muku tun yana Galili

7. cewa, ‘Lalle ne a ba da Ɗan Mutum ga mutane masu zunubi, a gicciye shi, a rana ta uku kuma ya tashi’.”

8. Sai suka tuna da maganarsa.

9. Da suka dawo daga kabarin suka shaida wa goma sha ɗayan nan, da kuma duk sauransu, dukan waɗannan abubuwa.

10. To, Maryamu Magadaliya, da Yuwana, da Maryamu uwar Yakubu, da kuma sauran matan da suke tare da su, su ne suka gaya wa manzannin waɗannan abubuwa.

11. Su kuwa sai maganan nan ta zama musu kamar zance ne kawai, suka ƙi gaskatawa.

12. Amma Bitrus ya tashi, ya doshi kabarin da gudu. Ya duƙa, ya leƙa a ciki, ya ga likkafanin lilin a ajiye waje ɗaya. Sai ya koma gida yana al'ajabin abin da ya auku.

13. A ran nan kuma sai ga waɗansu biyu suna tafiya wani ƙauye, mai suna Imuwasu, nisansa daga Urushalima kuwa kusan mil bakwai ne.

Karanta cikakken babi Luk 24