Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

Zab 44:3-15 Littafi Mai Tsarki (HAU)

3. Ba da takubansu suka ci ƙasar ba,Ba kuwa da ikonsu suka rinjayi ƙasar ba,Amma da ikonka ne da kuma ƙarfinka,Ta wurin tabbatar musu kana tare da su,Kana nuna musu kana ƙaunarsu.

4. “Ya Allah, kai ne Sarkina,Ka ba jama'arka nasara.

5. Da ikonka muka kori abokan gābanmu,Saboda kasancewarka tare da muMuka rinjayi magabtanmu.

6. Ban dogara ga bakana ba,Takobina kuwa ba zai cece ni ba.

7. Amma ka cece mu daga abokan gābanmu,Ka kori waɗanda suke ƙinmu.

8. Za mu yabe ka kullum,Mu yi maka godiya har abada.”

9. Amma yanzu, ya Allah, ka yashe mu,Ka bari aka kore mu,Ba ka ƙara fita ka yi tafiya tare da sojojinmu ba.

10. Ka sa muka gudu daga gaban abokan gābanmu,Suka ƙwace abin da muke da shi.

11. Ka bari aka yanyanka mu kamar tumaki,Ka warwatsar da mu a baƙuwar ƙasa.

12. Ka sayar da jama'arkaA bakin 'yan kuɗi ƙalilan,Ba ka ci ribar cinikin ba.

13. Maƙwabtanmu suna yi mana dariya saboda kai,Suna yi mana ba'a, sun maishe mu abin wasa.

14. Ka maishe mu abin raini a wurin arna,Suna kaɗa mana kai, suna raina mu.

15. Kullum a cikin kunya nake,Kunya ta lulluɓe ni ɗungum,

Karanta cikakken babi Zab 44