Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

M. Sh 31:1-7 Littafi Mai Tsarki (HAU)

1. Sai Musa ya ci gaba da yi wa dukan Isra'ilawa magana.

2. Ya ce, “Yau shekarata ɗari da ashirin ne, ba na iya kaiwa da komowa. Ubangiji kuwa ya ce mini, ‘Ba za ka haye wannan Urdun ba.’

3. Ubangiji Allahnku shi ne zai yi gaba ya haye, ya hallaka al'umman da take gabanku don ku ci su. Joshuwa ne zai shugabance ku, ya haye kamar yadda Ubangiji ya faɗa.

4. Ubangiji zai yi musu kamar yadda ya yi wa Sihon da Og, sarakunan Amoriyawa, da ƙasarsu, sa'ad da ya hallaka su.

5. Ubangiji zai bashe su a gare ku. Za ku yi musu kamar yadda dā na umarce ku.

6. Ku ƙarfafa, ku yi ƙarfin hali, kada ku ji tsoro, ko ku firgita saboda su, gama Ubangiji Allahnku yana tare da ku. Ba zai kunyatar da ku ba, ba kuwa zai yashe ku ba.”

7. Sai Musa ya kira Joshuwa, ya yi masa magana a gaban dukan jama'ar Isra'ila, ya ce, “Ka ƙarfafa, ka yi ƙarfin hali, gama kai ne za ka kai wannan jama'a cikin ƙasar da Ubangiji ya rantse zai ba kakanninsu. Kai ne za ka ba su ita gādo.

Karanta cikakken babi M. Sh 31