Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

K. Mag 19:6-26 Littafi Mai Tsarki (HAU)

6. Kowa na ƙoƙari ya sami farin jini wurin manyan mutane, kowa na so a ce shi abokin mutumin nan ne, mai yawan alheri.

7. 'Yan'uwan matalauci ba su bukatarsa, ba abin mamaki ba ne ya rasa abokai. Kome ƙoƙarin da zai yi ba zai sami ko ɗaya ba.

8. Ka yi wa kanka gatanci, ka koyi dukan abin da kake iyawa, sa'an nan ka tuna da abin da ka koya, za ka arzuta.

9. Ba wanda zai faɗi ƙarya a majalisa ya rasa shan hukunci, maƙaryaci, tasa ta ƙare.

10. Ko kusa wawaye ba za su yi zaman jin daɗi ba, haka nan kuma bayi ba za su yi mulki a kan iyayengijinsu ba.

11. Mutum mai hankali yake danne fushinsa. Lokacin da wani ya cuce ka, abin kirki ne, ka yi kamar ba ka kula da shi ba.

12. Hasalar sarki kamar rurin zaki ne, amma alherinsa kamar saukar ruwan sama ne.

13. Dakikin ɗa yana jawo wa mahaifinsa lalacewa, mace mai mita tana kama da ɗiɗɗigar ruwa.

14. Mutum na iya cin gādon gida da kuɗi daga wurin iyayensa, amma Ubangiji ne kaɗai yake ba shi mace mai hankali.

15. Rago, yi ta ragwancinka ka yi ta sharar barci, amma kai za ka sha yunwa.

16. Ka kiyaye umarnai za ka rayu, in ka ƙi binsu kuwa za ka mutu.

17. Sa'ad da ka bayar ga matalauci kamar ka ba Ubangiji rance ne, gama Ubangiji zai sāka maka.

18. Ka yi wa 'ya'yanka tarbiyya tun suna ƙanana yadda za su iya koyo. Idan ba ka yi haka ba, ka taimaka wajen lalacewarsu ke nan.

19. Idan mutum mai zafin rai ne, ƙyale shi ya sha sakamakonsa. Idan ka fisshe shi daga cikin wahala sau ɗaya, sai ka sāke yi.

20. Ka saurari shawara, ka yarda ka koya, wata rana za ka zama mai hikima.

21. Mutum ya iya shirya dabaru iri iri, amma sai nufin Ubangiji ne zai tabbata.

22. Abin kunya ne mutum ya zama mai haɗama, matalauci kuma ya fi maƙaryaci.

23. Ka yi tsoron Ubangiji za ka yi tsawon rai, ka kuma sami biyan bukata, ba abin da zai cuce ka.

24. Waɗansu mutane sun cika lalaci, ko abincinsu ba su iya taunawa.

25. Za a hukunta mai fāriya saboda ya zama ishara ga mutanen da ba su san kome ba, mutum mai hikima yakan koya sa'ad da aka tsauta masa.

26. Sai marar kunya, marar mutunci suke wulakanta mahaifinsa, ko ya kori mahaifiyarsa daga gidansa.

Karanta cikakken babi K. Mag 19