Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

Irm 49:3-17 Littafi Mai Tsarki (HAU)

3. “Ki yi kuka, ya Heshbon, gama Ai tazama kufai!Ku yi kuka, ku mutanen Rabba, kusa tufafin makoki.Ku yi gudu, kuna kai da kawowa acikin garuka,Gama za a kai Milkom bauta tare dafiristocinsa da wakilansa.

4. Me ya sa kuke taƙama daƙarfinku,Ƙarfinku da yake ƙarewa, ku mutanemarasa aminci?Kun dogara ga dukiyarku,Kuna cewa, ‘Wane ne zai iya gāba damu?’

5. Ga shi, zan kawo muku razana dagawaɗanda suke kewaye da ku,Za a kore ku, kowane mutum zaikama gabansa,Ba wanda zai tattara 'yan gudunhijira.Ni Ubangiji Allah Mai Rundunana faɗa.

6. “Amma daga baya zan saAmmonawa su wadata kuma,Ni Ubangiji na faɗa.”

7. Ga abin da Ubangiji Mai Rundunaya faɗa a kan Edom,“Ba hikima kuma a cikin Teman?Shawara ta lalace a wurin masubasira?Hikima ta lalace ne?

8. Ku mazaunan Dedan, ku juya, kugudu,Ku ɓuya cikin zurfafa,Gama zan kawo masifa a kan IsuwaA lokacin da zan hukunta shi,

9. Idan masu tsinkar 'ya'yan inabi sunzo wurinkaBa za su rage abin kala ba?Idan kuma ɓarayi sun zo da dare,Za su ɗauki iyakacin abin da suke sokurum.

10. Amma na tsiraita Isuwa sarai,Na buɗe wuraren ɓuyarsa,Har bai iya ɓoye kansa ba,An hallakar da mutanen IsuwaTare da 'yan'uwansa damaƙwabtansa,Ba wanda ya ragu.

11. Ka bar marayunka, ni zan rayar dasu.Matanka da mazansu sun mutu,Sai su dogara gare ni.”

12. Ubangiji ya ce, “Ga shi, waɗanda ba a shara'anta su ga shan ƙoƙon hukunci ba, za su sha shi, to, kai za ka kuɓuta? Ba za ka kuɓuta ba, amma lalle za ka sha shi!

13. Gama ni Ubangiji na rantse da zatina, cewa Bozara za ta zama abar tsoro, da abar dariya, da kufai, da abar la'ana. Dukan garuruwanta za su zama kufai har abada.”

14. Irmiya ya ce,“Na karɓi saƙo daga wurinUbangiji.An aiki jakada a cikin al'ummaicewa,‘Ku tattara kanku, ku zo ku yi gābada ita,Ku tasar mata da yaƙi!’

15. Gama ga shi, zan maishe kiƙanƙanuwa cikin al'ummai,Abar raini a wurin mutane.

16. Tsoronki da ake ji da girmankankisun ruɗe ki,Ke da kike zaune a kogon dutse, akan tsauni,Ko da yake kin yi gidanki can samakamar gaggafa,Duk da haka zan komar da ke ƙasa,Ni Ubangiji na faɗa.”

17. Ubangiji ya ce, “Edom za ta lalace, duk wanda ya bi ta wurin zai gigice, ya yi tsaki saboda dukan masifunta.

Karanta cikakken babi Irm 49