Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

Irm 48:33-45 Littafi Mai Tsarki (HAU)

33. An ɗauke farin ciki da murna dagaƙasa mai albarka ta Mowab,Na hana ruwan inabi malala dagawurin matsewarsa,Ba wanda yake matse shi, yana ihu namurna,Ihun da ake yi ba na murna ba ne.

34. “Mutanen Heshbon da na Eleyale suna kururuwa ana iya jin kururuwansu a Yahaza. Ana iya jinta kuma a Zowar, da Horonayim, da Eglat-shelishiya. Har ma ruwan Nimra ya ƙafe.

35. Zan hana mutanen Mowab miƙa hadayu na ƙonawa a tuddai, da miƙa wa gumakansu sadaka, ni Ubangiji na faɗa.

36. “Zuciyata tana makoki domin Mowab da Kir-heres kamar wanda yake kukan makoki da sarewa saboda wadatarsu ta ƙare.

37. Gama kowa ya aske kansa da gemunsa, sun tsattsage hannuwansu. Kowa kuma ya sa rigar makoki.

38. Ba abin da ake yi a bisa kan soraye da dandali na Mowab sai baƙin ciki, gama na farfashe Mowab kamar tulun da ba a so, ni Ubangiji na faɗa.

39. An farfashe Mowab, ta yi kuka, ta kunyata! Ta zama abin dariya da abin tsoro ga waɗanda suke kewaye da ita.

40. “Ni Ubangiji na ce,Wani zai yi firiya da sauri kamargaggafa,Zai shimfiɗa fikafikansa a kanMowab.

41. Za a ci garuruwa da kagarai dayaƙi,A wannan rana zukatan sojojinMowabZa su zama kamar zuciyar macen datake naƙuda.

42. Za a hallaka Mowab daga zamanal'umma,Domin ta tayar wa Ubangiji.

43. Tsoro, da rami, da tarko sunajiranku,Ya mazaunan Mowab,Ni Ubangiji na faɗa.

44. Wanda ya guje wa tsoro,Zai fāɗa a rami,Wanda kuma ya fito daga cikinrami,Tarko zai kama shi.Gama na sa wa Mowab lokacin dazan hukunta ta,Ni Ubangiji na faɗa.

45. “A ƙarƙashin inuwar Heshbon 'yangudun hijira suna tsaye ba ƙarfi.Gama wuta ta ɓullo daga Heshbon,Harshen wuta kuma ya fito dagaSihon,Ta ƙone goshin Mowab daƙoƙwan kai na 'yan tayarwa.

Karanta cikakken babi Irm 48