Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

Irm 4:5-15 Littafi Mai Tsarki (HAU)

5. “Ku yi shela a cikin Yahuza,Ku ta da murya a Urushalima, kuce,‘Ku busa ƙaho a dukan ƙasar!’Ku ta da murya da ƙarfi, ku ce,‘Ku tattaru, mu shiga birane masugaru.’

6. Ku ta da tuta wajen Sihiyona!Ku sheƙa a guje neman mafaka,kada ku tsaya!Gama zan kawo masifa da babbarhalaka daga arewa.

7. Zaki ya hauro daga cikinruƙuƙinsa,Mai hallaka al'ummai ya kamahanya,Ya fito daga wurin zamansa don yamai da ƙasarku kufai,Ya lalatar da biranenku, su zamakango, ba kowa.

8. Domin haka sai ku sa tufafinmakoki,Ku yi makoki ku yi kuka,Gama fushin Ubangiji bai rabu damu ba.”

9. Ubangiji ya ce, “A ranan nan, sarki da sarakuna, za su rasa ƙarfin hali, firistoci za su firgita, annabawa kuwa za su yi mamaki.”

10. Sai na ce, “Kaito, kaito, ya Ubangiji Allah, ka ruɗi jama'an nan da Urushalima, da ka ce musu, ‘Za ku zauna lafiya,’ amma ga shi, takobi zai sassare su.”

11. Lokaci yana zuwa da za a faɗa wa mutanen Urushalima cewa, “Iska mai zafi za ta huro daga tuddan hamada zuwa wajen jama'ata, ba domin a sheƙe ta ko a rairaye ta ba!

12. Wannan iska da za ta zo daga wurin Ubangiji, tana da mafificin ƙarfi. Yanzu fa zan yanke hukunci a kansu.”

13. Duba, ga abokin gāba yana zuwakamar gizagizai,Karusan yaƙinsa suna kama daguguwa,Dawakansa sun fi gaggafa sauri.Kaitonmu, mun shiga uku!

14. Ya Urushalima, ki wanke muguntadaga zuciyarki,Domin a cece ki,Har yaushe mugayen tunaninki za suyi ta zama a cikinki?

15. Gama wata murya daga Dan tafaɗa,Ta kuma yi shelar masifar da za tafito daga duwatsun Ifraimu.

Karanta cikakken babi Irm 4