Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

Irm 30:11-16 Littafi Mai Tsarki (HAU)

11. Gama ina tare da kai don in cece ka,Zan hallaka dukan al'ummai sarai,Inda na warwatsa ku.Amma ku ba zan hallaka ku ba,Zan hore ku da adalci,Ba yadda za a yi in ƙyale ku bahukunci,Ni Ubangiji na faɗa.”

12. Ubangiji ya ce,“Rauninku ba ya warkuwa,Mikinku kuwa mai tsanani neƙwarai.

13. Ba wanda zai kula da maganarku,Ba magani domin mikinku,Ba za ku warke ba.

14. Dukan masu ƙaunarku sun mantada ku,Ba su ƙara kulawa da ku,Domin na yi muku bugu irin namaƙiyi.Na yi muku horo irin na maƙiyimarar tausayi,Domin laifofinku masu girma ne,Domin zunubanku da yawa suke.

15. Don me kuke kuka a kanrauninku?Ciwonku ba zai warke ba.Saboda laifofinku masu girma ne,Domin zunubanku da yawa suke,Shi ya sa na yi muku waɗannanabubuwa.

16. Domin haka dukan waɗanda sukacinye ku, za a cinye su,Dukan maƙiyanku, kowane ɗayansuzai tafi bauta,Waɗanda suka washe ku, za a washesu.Dukan waɗanda suka kwashe kuganima, su ma za a kwashe suganima.

Karanta cikakken babi Irm 30