Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

Irm 23:10-17 Littafi Mai Tsarki (HAU)

10. Gama ƙasar cike take da mazinata,Saboda la'ana, ƙasar za ta yimakoki,Wuraren kiwo na jeji sun bushe,Manufarsu mugunta ce,Ba su mori ƙarfinsu a inda yakamata ba.

11. “Annabi da firist, dukansu biyumarasa tsoron Allah ne,Har a cikin Haikalina na tarar damuguntarsu.”Ubangiji ya faɗa.

12. “Saboda haka hanyarsu za ta zamada santsi da duhu,Inda za a runtume su, su fāɗi.Gama zai kawo musu masifa ashekarar da za su shahukuncinsu.”Ubangiji ya faɗa.

13. “A cikin annabawan Samariya,Na ga abu marar kyan gani.Da sunan Ba'al suke yin annabci,Suna ɓad da jama'ata Isra'ila

14. Amma cikin annabawa naUrushalima,Na ga abin banƙyama.Suna yin zina, suna ƙarya,Suna ƙarfafa hannuwan masu aikatamugunta,Saboda haka ba wanda ya juya gabarin muguntarsa,Dukansu suna kama da Saduma,Mazaunanta kuwa kamarGwamrata.”

15. Saboda haka ga abin da Ubangiji Mai Runduna ya ce a kan annabawa,“Ga shi, zan ciyar da su da abincimai ɗaci,In shayar da su da ruwan dafi.Daga wurin annabawan UrushalimaRashin tsoron Allah ya fito yamamaye dukan ƙasar.”

16. Ubangiji Mai Runduna ya ce wamazaunan Urushalima,“Kada ku kasa kunne ga maganarannabawa,Gama sukan cika kunnuwanku daƙarairayi.Suna faɗar ganin damarsu,Ba faɗar Ubangiji ba.

17. Suna ta faɗa wa waɗanda suke rainamaganar Ubangiji cewa,‘Za ku zauna lafiya!’Ga kowane mai bin nufin tattaurarzuciyarsa,‘Ba masifar da za ta same ka.’ ”

Karanta cikakken babi Irm 23