Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

Irm 13:12-23 Littafi Mai Tsarki (HAU)

12. “Sai ka faɗa musu wannan magana cewa, ‘Ni Ubangiji Allah na Isra'ila na ce, a cika kowane tulu da ruwan inabi.’ Su kuwa za su ce maka, sun sani sarai za a cika kowane tulu da ruwan inabi.

13. Sa'an nan za ka faɗa musu, Ubangiji ya ce, ‘Ga shi, zan sa dukan mazaunan ƙasar su bugu da ruwan inabi, wato sarakunan da suka hau gadon sarautar Dawuda, da firistoci, da annabawa, da dukan mazaunan Urushalima.

14. Zan sa su kara da junansu, iyaye maza da 'ya'yansu maza, in ji Ubangiji. Tausayi, ko juyayi, ko jinƙai ba za su sa in fasa hallaka su duka ba.’ ”

15. Ku kasa kunne, ku ji,Kada ku yi girmankai, gamaUbangiji ya yi magana.

16. Ku girmama Ubangiji Allahnku,Kafin ya kawo duhu,Kafin kuma ƙafafunku su yi tuntuɓea kan dutse, da duhu duhu,Sa'ad da kuke neman haske, sai yamaishe shi duhu,Ya maishe shi duhu baƙi ƙirin.

17. Amma idan ba za ku ji ba,Raina zai yi kuka a ɓoye sabodagirmankanku,Idanuna za su yi kuka ƙwarai, za suzub da hawaye,Domin an kai garken Ubangiji zuwabauta.

18. Ubangiji ya ce wa Irmiya,“Ka faɗa wa sarki da sarauniya,uwarsa, su sauka daga gadonsarautarsu,Domin an tuɓe kyakkyawan rawaninsarautarsu daga kansu.

19. An kulle biranen Negeb,Ba wanda zai buɗe su,Yahuza duka an kai ta zaman dole,Dukanta an kai ta zaman dole.

20. “Ku ta da idanunku, ku ga waɗandasuke zuwa daga arewa!Ina kyakkyawan garken nan da akaba ku?

21. Me za ku ce sa'ad da aka naɗa mukushugabanni,Waɗanda ku da kanku kuka koyamusu, suka zama abokanku?Ashe, azabai ba za su auko muku baKamar yadda sukan auko wa macemai naƙuda?

22. Idan kun ce a zuciyarku,‘Me ya sa waɗannan abubuwa sukasame mu?’Saboda yawan zunubanku ne,Shi ya sa an tone tsiraicinku,Aka wahalshe ku.

23. Mutumin Habasha zai iya sākelaunin fatar jikinsa?Ko kuwa damisa za ta iya sākedabbare-dabbarenta?Idan haka ne, ku kuma za ku iya yinnagarta,Ku da kuka saba da yin mugunta.

Karanta cikakken babi Irm 13