Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

Fit 19:21-23 Littafi Mai Tsarki (HAU)

21. Ubangiji ya ce wa Musa, “Sauka, ka faɗakar da jama'ar, don kada su ƙetare kan iyakar, su zo garin a kalli Ubangiji, da yawa daga cikinsu kuwa su mutu.

22. Ko firistocin da za su kusato Ubangiji, sai su tsarkake kansu, don kada in hukunta su.”

23. Musa ya ce wa Ubangiji, “Mutanen ba za su iya hawan dutsen Sina'i ba, gama kai da kanka ka umarce mu cewa, ‘Ku sa iyaka kewaye da dutsen, ku tsarkake shi.’ ”

Karanta cikakken babi Fit 19