Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

Ezra 8:18-20 Littafi Mai Tsarki (HAU)

18. Da yake Allah yana tare da mu, sai suka kawo mana mutum mai ganewa daga 'ya'yan Mali ɗan Lawi, ɗan Isra'ila. Sunan mutumin Sherebiya, da 'ya'yansa da 'yan'uwansa, su goma sha takwas ne.

19. Suka kuma kawo Hashabiya tare da Yeshaya daga 'ya'yan Merari. 'Yan'uwansa da 'ya'yansu su ashirin ne.

20. Da kuma ma'aikatan Haikali mutum ɗari biyu da ashirin, waɗanda Dawuda da ma'aikatansa suka keɓe domin su taimaki Lawiyawa. Aka ambaci waɗannan da sunayensu.

Karanta cikakken babi Ezra 8