Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

Ez 48:13-32 Littafi Mai Tsarki (HAU)

13. Gab da yankin firistoci, Lawiyawa za su sami rabo mai tsawon kamu dubu ashirin da dubu biyar [25,000], faɗi kuma kamu dubu goma [10,000]. Tsawonsa duka zai zama kamu dubu ashirin da dubu biyar [25,000], faɗi kuwa kamu dubu goma [10,000].

14. Daga cikinsa ba za su sayar ba, ko su musayar, ba kuma za su jinginar da wannan keɓaɓɓen yankin ƙasa ba, gama tsattsarka ne na Ubangiji.

15. “Ragowar yankin mai faɗin kamu dubu biyar [5,000], da tsawon kamu dubu ashirin da dubu biyar [25,000], zai zama hurumin birnin, inda za a yi gidaje da wurin kiwo. Birnin zai kasance a tsakiyar yankin.

16. Ga yadda girman birnin zai kasance, a wajen arewa kamu dubu huɗu da ɗari biyar [4,500], a wajen kudu kuwa kamu dubu huɗu da ɗari biyar [4,500], a wajen gabas kamu dubu huɗu da ɗari biyar [4,500], a wajen yamma kuma kamu dubu huɗu da ɗari biyar [4,500].

17. Birnin zai kasance da hurumi a kewaye da shi. A wajen gabas kamu metan da hamsin, a wajen yamma kamu metan da hamsin, a wajen kudu kamu metan da hamsin, a wajen arewa kuma kamu metan da hamsin.

18. Ragowar tsawon yankin da yake gab da tsattsarkan yankin, zai zama kamu dubu goma [10,000] a wajen gabas, a wajen yamma kamu dubu goma [10,000]. Amfanin da yankin zai bayar, zai zama abincin ma'aikatan birnin.

19. Ma'aikatan birnin za su samu daga dukan kabilan Isra'ila, za su noma yankin.

20. Dukan yankin da za ku keɓe zai zama murabba'i mai kamu dubu ashirin da dubu biyar [25,000], wato tsattsarkan yankin tare da hurumin birnin.

21. “Ragowar kowane gefe na tsattsarkan yankin da hurumin birnin, zai zama na sarki. Tun daga kamu dubu ashirin da dubu biyar [25,000] na tsattsarkan yankin, zuwa iyakar da take wajen gabas, daga kamu dubu ashirin da dubu biyar [25,000] kuma zuwa iyakar wajen yamma, hannun riga da yankunan kabilan zai zama na sarki. Tsattsarkan yankin da wuri mai tsarki na Haikali za su kasance a tsakiyarsa.

22. Rabon Lawiyawa da hurumin birnin za su kasance a tsakiyar yankin da yake na ɗan sarki. Yankin ɗan sarki zai kasance a tsakanin yankin Yahuza da yankin Biliyaminu.

23. “Sauran kabilan kuwa za su samu. Biliyaminu zai sami yankinsa daga gabas zuwa yamma.

24. Yankin Saminu yana kusa da yankin Biliyaminu daga gabas zuwa yamma.

25. Yankin Issaka yana kusa da yankin Saminu daga gabas zuwa yamma.

26. Yankin Zabaluna yana kusa da yankin Issaka daga gabas zuwa yamma.

27. Yankin Gad yana kusa da yankin Zabaluna daga gabas zuwa yamma.

28. “Kusa da yankin Gad zuwa kudu, iyakar za ta bi ta Tamar zuwa ruwan Meriba-kadesh, sa'an nan ta bi rafin Masar zuwa Bahar Rum.”

29. Ubangiji ya ce, “Wannan ita ce hanyar da za ku raba gādo tsakanin kabilan Isra'ila. Waɗannan kuwa su ne yankunansu, ni Ubangiji Allah na faɗa.”

30. “Ƙofofin birnin a gefen arewa, kamu dubu huɗu da ɗari biyar [4,500] ne.

31. Ƙofofi uku ne, wato Ƙofar Ra'ubainu, da Ƙofar Yahuza, da Ƙofar Lawi. Ana kiran sunayen ƙofofin birnin da sunayen kabilan Isra'ila.

32. A gefen gabas, kamu dubu huɗu ne da ɗari biyar [4,500]. Ƙofofi uku ne, wato Ƙofar Yusufu, da Ƙofar Biliyaminu, da Ƙofar Dan.

Karanta cikakken babi Ez 48