Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

Ez 47:3-8 Littafi Mai Tsarki (HAU)

3. Mutumin ya nufi wajen gabas da ma'auni a hannunsa, ya auna kamu dubu, sa'an nan ya sa ni in haye ruwan. Zurfin ruwan ya kama ni idon ƙafa.

4. Sai kuma ya auna kamu dubu, ya sa ni in haye ruwan. Zurfin ruwan kuwa ya kama ni gwiwa. Sai ya sāke auna kamu dubu, ya sa in haye ruwan, sai zurfin ruwan ya kai ga kama ni gindi.

5. Ya sāke auna kamu dubu kuma, sai ruwan ya zama kogi har ban iya in haye ba, gama ruwan ya hau, ya zama da zurfin da ya isa ninƙaya. Ya zama kogin da ba za a iya hayewa ba.

6. Sai ya tambaye ni, ya ce. “Ɗan mutum, ka ga wannan?”Sa'an nan ya komo da ni zuwa gāɓar kogin.

7. Sa'ad da nake tafiya, sai na ga itatuwa da yawa a kowace gāɓar kogin.

8. Ya kuma ce mini, “Wannan ruwa yana gangarowa zuwa wajen gabas har zuwa cikin Araba. Zai shiga ruwan teku marar gudu, ruwan tekun kuwa zai zama ruwan daɗi.

Karanta cikakken babi Ez 47