Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

Ez 38:15-20 Littafi Mai Tsarki (HAU)

15. Za ka taso daga wurin da kake, can ƙurewar arewa, da jama'a mai yawa tare da kai, babbar rundunar mayaƙa mai ƙarfi, dukansu a kan dawakai.

16. Za ka zo ka yi yaƙi da mutanen Isra'ila, za ka rufe su kamar yadda girgije yakan rufe sararin sama. A kwanaki na ƙarshe zan kawo ka ka yi yaƙi da ƙasata domin al'ummai su san ni sa'ad da na bayyana tsarkina a gabansu ta wurin abin da ka yi.”’

17. Ubangiji Allah ya ce, “Kai ne wanda na yi magana a kanka a zamanin dā ta wurin bayina annabawan Isra'ila, cewa a shekaru masu zuwa zan kawo ka, ka yaƙe su.

18. Amma a wannan rana sa'ad da Gog zai kawo wa ƙasar Isra'ila yaƙi, ni Ubangiji Allah zan hasala.

19. Gama a kishina da zafin hasalata na hurta, cewa a wannan rana za a yi babbar girgiza a ƙasar Isra'ila.

20. Kifayen teku, da tsuntsayen sararin sama, da bisashe, da dukan masu rarrafe, da dukan mutanen da suke duniya, za su yi makyarkyata a gabana. Za a jefar da duwatsu ƙasa, tsaunuka za su fādi, kowane bango zai rushe.

Karanta cikakken babi Ez 38