Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

Ez 38:1-9 Littafi Mai Tsarki (HAU)

1. Ubangiji ya yi magana da ni, ya ce,

2. “Ɗan mutum, ka fuskanci Gog na ƙasar Magog, babban shugaban Rosh, da Meshek, da Tubal, ka yi annabci a kansa,

3. ka ce Ubangiji Allah ya ce, ‘Ga shi, ina gaba da kai, ya Gog, babban shugaban Rosh, da Meshek, da Tubal.

4. Zan juyar da kai, in sa ƙugiyoyi cikin muƙamuƙanka, in fitar da kai, da dukan sojojinka, da dawakai da mahayansu. Su babbar runduna ce saye da makamai, wato garkuwoyi, da takuba a zāre,

5. mutanen Farisa, da Habasha, duk da Fut. Dukansu suna saye da garkuwa da kwalkwali,

6. da Gomer tare da dukan sojojinsa, da Bet-togarma daga ƙurewar arewa, da dukan sojojinsa, su jama'a mai yawa, suna tare da kai.

7. Ka shirya, ka kuma zama da shiri, kai da dukan rundunar da suka tattaru kewaye da kai, ka zama ɗan tsaronsu.

8. Bayan kwanaki masu yawa zan ziyarce ka, a cikar waɗannan shekaru, za ka koma ƙasar duwatsun Isra'ila, wadda ta farfaɗo daga masifar yaƙin da ta sha, ƙasa inda jama'a suka tattaru daga sauran al'umma masu yawa, wadda a dā ta yi ta lalacewa, sai da aka fito da mutanenta daga cikin al'ummai, yanzu kuwa dukansu suna zaman lafiya.

9. Za ka ci gaba, kana zuwa kamar hadiri, za ka rufe ƙasar kamar gizagizai, kai da rundunarka, da jama'a masu yawa tare da kai.”’

Karanta cikakken babi Ez 38