Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

Ez 33:20-29 Littafi Mai Tsarki (HAU)

20. Amma duk da haka kun ce, ‘Hanyar Ubangiji ba daidai ba ce.’ Ya mutanen Isra'ila, zan hukunta kowane ɗayanku gwargwadon ayyukansa.”

21. A rana ta biyar ga watan goma, a shekara ta goma sha biyu ta zaman bautar talala da aka kai mu, sai wani ɗan gudun hijira daga Urushalima ya zo wurina, ya ce, “Birnin ya fāɗi.”

22. A maraicen da ya wuce kafin ɗan gudun hijirar ya iso, Ubangiji ya ƙarfafa ni, ya kuma buɗe bakina a lokacin da mutum ya zo wurina da safe. Bakina kuwa ya buɗe, ban zama bebe ba kuma.

23. Ubangiji kuma ya yi magana da ni, ya ce,

24. “Ɗan mutum, mazaunan wuraren nan da aka lalatar a ƙasar Isra'ila, suna cewa, ‘Ibrahim shi kaɗai ne, duk da haka an ba shi ƙasar duka, balle fa mu da muke da yawa, lalle ƙasar tamu ce.’

25. “Domin haka, sai ka faɗa musu, ‘Ubangiji Allah ya ce, “Kuna cin nama da jininsa, kuna bautar gumaka, kuna kuma yin kisankai, da haka za ku mallaki ƙasar?

26. Kun sa dogararku ga takobi kuna aikata abubuwan bankyama, kowannenku kuma yana zina da matar maƙwabcinsa, da haka za ku iya mallakar ƙasar?”’

27. “Ka faɗa musu, ‘Ubangiji ya ce, “Hakika, waɗanda suke a wuraren da aka lalatar, za a kashe su da takobi, wanda kuma yake a saura zan sa namomin jeji su cinye shi. Waɗanda kuma suke cikin kagara, da kogwannin duwatsu, annoba za ta kashe su.

28. Zan mai da ƙasar kufai marar amfani, fariya za ta ƙare. Tuddan Isra'ila za su zama kufai, ba wanda zai ratsa ta cikinsu.

29. Sa'an nan za su sani ni ne Ubangiji, sa'ad da na mai da ƙasar kufai marar amfani saboda dukan ayyukansu na banƙyama.” ’ ”

Karanta cikakken babi Ez 33