Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

Ez 28:16-26 Littafi Mai Tsarki (HAU)

16. A wurin yawan kasuwancinka,Ka yi rikici da yawa har ka yi zunubi.Don haka na jefar da kai daga dutsen AllahKamar ƙazantaccen abu.Na hallaka ka daga tsakiyar duwatsu na wuta,Kai mala'ikan tsaro.

17. Zuciyarka ta yi alfarma saboda kyanka,Ka lalatar da hikimarka ta wurin nuna darajar kanka.Na jefar da kai zuwa ƙasa,Na tone asirinka a gaban sarakuna don su kallace ka.

18. Saboda yawan muguntarka da rashin gaskiyarka cikin kasuwanci,Ka ƙazantar da tsarkakakkun wurarenka.Don haka na sa wuta ta fito daga cikinka, ta cinye ka,Na maishe ka toka a bisa ƙasa a kan idon dukan waɗanda suka kallace ka.

19. Dukan waɗanda suka san ka a cikin al'ummaiZa su gigice saboda masifar da ta auko maka,Za ka zama barazana ga al'ummai,Ba za ka ƙara kasancewa ba har abada.”’

20. Ubangiji ya yi magana da ni kuma, ya ce,

21. “Ɗan mutum, ka fuskanci Sidon, ka yi annabci a kanta.

22. Ka ce, Ubangiji Allah ya ce,‘Duba, ina gāba da ke, ya Sidon,Zan bayyana ikona a cikinki,Za su sani ni ne Ubangiji sa'ad da na hukunta ta,Na bayyana tsarkina a cikinta.

23. Zan aukar mata da annoba da jini a titunanta.Waɗanda za a ji musu rauni da takobiZa su fāɗi matattu a tsakiyarta.Za a tasar mata a kowane waje.Sa'an nan za su sani ni ne Ubangiji.’ ”

24. “ ‘A kan mutanen Isra'ila kuwa, al'ummai da suke kewaye da su, waɗanda suka raina su, ba za su ƙara zamar musu kamar sarƙaƙƙiya da ƙaya ba. Sa'an nan za su sani ni ne Ubangiji Allah.’

25. “Ubangiji Allah ya ce, ‘Sa'ad da na tattara mutanen Isra'ila daga cikin sauran al'umma, inda na watsar da su, na kuma bayyana tsarkina a cikinsu a kan idon al'ummai, sa'an nan za su zauna a ƙarsarsu wadda na ba bawana Yakubu.

26. Za su zauna lafiya a cikinta, za su gina gidaje, su yi gonakin inabi. Za su zauna gonakin inabi. Za su zauna lafiya sa'ad da na hukunta maƙwabtansu waɗanda suka wulakanta su. Sa'an nan za su sani ni ne Ubangiji Allahnsu.’ ”

Karanta cikakken babi Ez 28