Surori

  1. 1
  2. 2
  3. 3
  4. 4
  5. 5
  6. 6
  7. 7
  8. 8
  9. 9
  10. 10
  11. 11
  12. 12
  13. 13
  14. 14
  15. 15
  16. 16
  17. 17
  18. 18
  19. 19
  20. 20
  21. 21
  22. 22
  23. 23
  24. 24
  25. 25
  26. 26
  27. 27
  28. 28
  29. 29
  30. 30
  31. 31
  32. 32
  33. 33
  34. 34
  35. 35
  36. 36
  37. 37
  38. 38
  39. 39
  40. 40
  41. 41
  42. 42
  43. 43
  44. 44
  45. 45
  46. 46
  47. 47
  48. 48

Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

Ez 28 Littafi Mai Tsarki (HAU)

Annabci a kan Sarkin Taya

1. Ubangiji ya yi magana da ni ya ce,

2. “Dan mutum, ka faɗa wa Sarkin Taya, cewa Ubangiji Allah ya ce,‘Da yake zuciyarka ta cika da alfarma,Har ka ce kai allah ne,Kana zaune a mazaunin allah, kana zaune a tsakiyar tekuna,To, kai mutum ne kawai, ba allah ba,Ko da yake ka aza kanka mai hikima ne kamar Allah.

3. Lalle ka fi Daniyel hikima,Ba asirin da yake ɓoye a gare ka.

4. Ta wurin hikimarka da ganewarka ka samo wa kanka dukiya,Ka tattara zinariya da azurfa a baitulmalinka.

5. Saboda yawan hikimarka na yin kasuwanci, ka ƙara dukiyarka,Sai dukiyarka ta sa zuciyarka ta cika da alfarma.’

6. “Saboda haka Ubangiji Allah ya ce,‘Da yake ka aza kanka mai hikima ne kamar Allah,

7. Don haka zan tura baƙi a kanka,Waɗanda suka fi mugunta cikin sauran al'umma.Za su zare takubansu a kan kyakkyawar hikimarka,Za su ɓara darajarka.

8. Za su jefar da kai cikin rami,Za ka mutu kamar waɗanda suka mutu a tsakiyar teku.

9. Har yanzu za ka ce kai allah ne a gaban waɗanda suke ji maka rauni, Ko da yake kai mutum ne kawai, ba Allah ba?

10. Za ka yi mutuwa irin ta kare ta hannun baƙi,Gama ni Ubangiji Allah na faɗa.’ ”

Makoki a kan Sarkin Taya

11. Ubangiji kuma ya yi magana da ni ya ce,

12. “Ɗan mutum, ka yi makoki a kan Sarkin Taya, ka ce Ubangiji Allah ya ce,‘Kai cikakke ne, cike da hikima da jamali!

13. Kana cikin Aidan, gonar Allah.An yi maka sutura da kowane irin dutse mai daraja,Tare da zinariya.Kana da molo da abin busa.A ranar da aka halicce kaSuna nan cikakku.

14. Na keɓe ka ka zama mala'ika mai tsaro,Kana bisa tsattsarkan dutsen Allah,Ka yi tafiya a tsakiyar duwatsu na wuta.

15. Daga ranar da aka halicce ka ba ka da laifi cikin al'amuranka,Sai ran da aka iske mugunta a cikinka.

16. A wurin yawan kasuwancinka,Ka yi rikici da yawa har ka yi zunubi.Don haka na jefar da kai daga dutsen AllahKamar ƙazantaccen abu.Na hallaka ka daga tsakiyar duwatsu na wuta,Kai mala'ikan tsaro.

17. Zuciyarka ta yi alfarma saboda kyanka,Ka lalatar da hikimarka ta wurin nuna darajar kanka.Na jefar da kai zuwa ƙasa,Na tone asirinka a gaban sarakuna don su kallace ka.

18. Saboda yawan muguntarka da rashin gaskiyarka cikin kasuwanci,Ka ƙazantar da tsarkakakkun wurarenka.Don haka na sa wuta ta fito daga cikinka, ta cinye ka,Na maishe ka toka a bisa ƙasa a kan idon dukan waɗanda suka kallace ka.

19. Dukan waɗanda suka san ka a cikin al'ummaiZa su gigice saboda masifar da ta auko maka,Za ka zama barazana ga al'ummai,Ba za ka ƙara kasancewa ba har abada.”’

Annabci a kan Sidon

20. Ubangiji ya yi magana da ni kuma, ya ce,

21. “Ɗan mutum, ka fuskanci Sidon, ka yi annabci a kanta.

22. Ka ce, Ubangiji Allah ya ce,‘Duba, ina gāba da ke, ya Sidon,Zan bayyana ikona a cikinki,Za su sani ni ne Ubangiji sa'ad da na hukunta ta,Na bayyana tsarkina a cikinta.

23. Zan aukar mata da annoba da jini a titunanta.Waɗanda za a ji musu rauni da takobiZa su fāɗi matattu a tsakiyarta.Za a tasar mata a kowane waje.Sa'an nan za su sani ni ne Ubangiji.’ ”

Isra'ila Za ta Sami Albarka

24. “ ‘A kan mutanen Isra'ila kuwa, al'ummai da suke kewaye da su, waɗanda suka raina su, ba za su ƙara zamar musu kamar sarƙaƙƙiya da ƙaya ba. Sa'an nan za su sani ni ne Ubangiji Allah.’

25. “Ubangiji Allah ya ce, ‘Sa'ad da na tattara mutanen Isra'ila daga cikin sauran al'umma, inda na watsar da su, na kuma bayyana tsarkina a cikinsu a kan idon al'ummai, sa'an nan za su zauna a ƙarsarsu wadda na ba bawana Yakubu.

26. Za su zauna lafiya a cikinta, za su gina gidaje, su yi gonakin inabi. Za su zauna gonakin inabi. Za su zauna lafiya sa'ad da na hukunta maƙwabtansu waɗanda suka wulakanta su. Sa'an nan za su sani ni ne Ubangiji Allahnsu.’ ”