Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

Dan 9:7-10 Littafi Mai Tsarki (HAU)

7. Ya Ubangiji, kai mai adalci ne, amma mu sai kunya, kamar yadda yake a yau ga mutanen Yahuza, da mazaunan Urushalima da dukan Isra'ilawa, waɗanda suke kusa da waɗanda suke nesa a dukan ƙasashen da ka kora su saboda rashin amincin da suka yi maka.

8. Ya Ubangiji kunya ta rufe mu, mu da sarakunanmu, da shugabanninmu, da kakanninmu, saboda mun yi maka zunubi.

9. Ubangiji Allahnmu mai jinƙai ne mai gafara, amma mu, mun tayar masa.

10. Ba mu yi biyayya ga Ubangiji Allahnmu ta wurin kiyaye dokokinsa ba, waɗanda ya ba mu ta hannun bayinsa annabawa.

Karanta cikakken babi Dan 9