Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

Dan 4:32-36 Littafi Mai Tsarki (HAU)

32. Za a kuma kore ka daga cikin mutane zuwa jeji, ka zauna tare da namomin jeji. Za ka ci ciyawa kamar sa har shekara bakwai cur, sa'an nan za ka gane Maɗaukaki ne yake sarautar 'yan adam, yakan kuma ba da ita ga wanda ya ga dama.”

33. Nan take sai abin da aka faɗa a kan Nebukadnezzar ya tabbata. Aka kore shi daga cikin mutane. Ya shiga cin ciyawa kamar sa. Jikinsa ya jiƙe da raɓa, har gashinsa ya yi tsawo kamar gashin gaggafa, akaifunsa kuma suka yi tsawo kamar na tsuntsu.

34. “A ƙarshen kwanakin, sai ni Nebukadnezzar, na ɗaga ido sama, sai hankalina ya komo mini, na ɗaukaka Maɗaukaki, na yabe shi, na girmama shi wanda yake rayayye har abada.“Gama mulkinsa madawwamin mulki ne,Sarautarsa kuwa daga zamani zuwa zamani.

35. Dukan mazaunan duniya ba a bakin kome suke a gare shi ba.Yakan yi yadda ya nufa da rundunar sama da mazaunan duniya,Ba mai hana shi, ba kuma mai ce masa, ‘Me kake yi?’

36. “A lokacin nan hankalina ya komo mini, sai aka mayar mini da masarautata mai daraja, da martabata, da girmana. 'Yan majalisata da fādawana suka nemo ni. Aka maido ni kan gadon sarautata da daraja fiye da ta dā.

Karanta cikakken babi Dan 4