Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

2 Tar 18:5-14 Littafi Mai Tsarki (HAU)

5. Ahab kuwa ya tattara annabawa, mutum ɗari huɗu, ya ce musu, “Mu je mu faɗa wa Ramot-gileyad da yaƙi, ko in haƙura?”Sai suka ce, “Ka tafi, gama Allah zai ba da ita a hannun sarki.”

6. Amma Yehoshafat ya ce, “Ba wani annabin Ubangiji a nan wanda za mu tambaye shi kuma?”

7. Sai Sarkin Isra'ila ya ce wa Yehoshafat, “Akwai sauran mutum guda wanda za mu iya neman nufin Ubangiji daga gare shi, shi ne Mikaiya, ɗan Imla, amma na ƙi shi saboda ba ya yin annabcin kirki a kaina, sai dai na rashin alheri kullum.”Amma Yehoshafat ya ce, “Kada sarki ya faɗi haka.”

8. Sa'an nan Sarkin Isra'ila ya kira wani jarumi ya ce masa, “Maza ka kawo Mikaiya ɗan Imla.”

9. A sa'an nan Sarkin Isra'ila, da Yehoshafat, Sarkin Yahuza, suna zaune kowa a gadon sarautarsa, kowane ya caɓa ado, suna kuwa zaune a filin da yake ƙofar Samariya. Dukan annabawa kuwa suna ta yin annabci a gabansu.

10. Sai Zadakiya ɗan Kena'ana ya yi ƙahonin ƙarfe, ya ce, “Ga abin da Ubangiji ya ce, ‘Da waɗannan za ka sassoki Suriyawa har su hallaka!’ ”

11. Dukan annabawa kuma suka yi annabci, suna cewa, “Ka haura zuwa Ramot-gileyad ka ci nasara, gama Ubangiji zai ba da ita a hannun sarki.”

12. Jarumin fa da ya je ya kira Mikaiya ɗin, ya ce masa, “Ka kula fa, dukan maganganun da annabawa suke yi, sun yi wa sarki daɗi. Don haka kai ma ka yi maganar da za ta gamshi sarki kamar yadda suka yi.”

13. Amma Mikaiya ya ce, “Na rantse da Ubangiji abin da Allahna ya faɗa mini, shi zan faɗa.”

14. Da Mikaiya ya zo gaban sarki, sai sarki ya ce masa, “Mikaiya, mu haura zuwa Ramot-gileyad mu fāɗa mata da yaƙi, ko in haƙura?”Mikaiya kuwa ya amsa, ya ce, “Ka haura, gama za ka ci nasara, gama za a bashe su a hannunka.”

Karanta cikakken babi 2 Tar 18