Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

2 Tar 18:1-10 Littafi Mai Tsarki (HAU)

1. Yehoshafat ya arzuta, ya kuma sami ɗaukaka sai ya yi ma'amala da Ahab ta wurin aurayya.

2. Bayan 'yan shekaru sai ya kai wa Ahab ziyara a Samariya. Ahab kuwa ya yanka tumaki masu yawan gaske, da bijimai da yawa, domin Yehoshafat da mutanen da suke tare da shi. Ahab ya rinjaye shi don su fāɗa wa Ramot-gileyad da yaƙi.

3. Sai Ahab, Sarkin Isra'ila, ya ce wa Yehoshafat, Sarkin Yahuza, “Za ka tafi tare da ni zuwa Ramot-gileyad?”Sai ya amsa, ya ce, “Ni ma kamarka ne, jama'ata kuma kamar jama'arka ce, za mu je yaƙin tare da kai.”

4. Yehoshafat kuma ya ce wa Sarkin Isra'ila, “Sai ka nemi faɗar Ubangiji tukuna.”

5. Ahab kuwa ya tattara annabawa, mutum ɗari huɗu, ya ce musu, “Mu je mu faɗa wa Ramot-gileyad da yaƙi, ko in haƙura?”Sai suka ce, “Ka tafi, gama Allah zai ba da ita a hannun sarki.”

6. Amma Yehoshafat ya ce, “Ba wani annabin Ubangiji a nan wanda za mu tambaye shi kuma?”

7. Sai Sarkin Isra'ila ya ce wa Yehoshafat, “Akwai sauran mutum guda wanda za mu iya neman nufin Ubangiji daga gare shi, shi ne Mikaiya, ɗan Imla, amma na ƙi shi saboda ba ya yin annabcin kirki a kaina, sai dai na rashin alheri kullum.”Amma Yehoshafat ya ce, “Kada sarki ya faɗi haka.”

8. Sa'an nan Sarkin Isra'ila ya kira wani jarumi ya ce masa, “Maza ka kawo Mikaiya ɗan Imla.”

9. A sa'an nan Sarkin Isra'ila, da Yehoshafat, Sarkin Yahuza, suna zaune kowa a gadon sarautarsa, kowane ya caɓa ado, suna kuwa zaune a filin da yake ƙofar Samariya. Dukan annabawa kuwa suna ta yin annabci a gabansu.

10. Sai Zadakiya ɗan Kena'ana ya yi ƙahonin ƙarfe, ya ce, “Ga abin da Ubangiji ya ce, ‘Da waɗannan za ka sassoki Suriyawa har su hallaka!’ ”

Karanta cikakken babi 2 Tar 18