Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

2 Tar 13:13-16 Littafi Mai Tsarki (HAU)

13. Ashe, Yerobowam ya riga ya sa 'yan kwanto, su yi musu yankan baya. Ƙungiyar mayaƙan Isra'ila tana fuskantar ta Yahuza, 'yan kwanto kuma suna bayansu.

14. Da Yahuza suka duba, sai ga yaƙi a gabansu da bayansu. Sai suka yi kuka ga Ubangiji, firistoci kuma suka busa ƙaho.

15. Mutanen Yahuza suka yi kūwwar yaƙi. Da suka yi kuwwar yaƙin sai Ubangiji ya sa Yerobowam da dukan jama'ar Isra'ila su gudu a gaban Abaija da Yahuza.

16. Mutanen Isra'ila kuwa suka gudu a gaban Yahuza, Allah ya bashe su a hannunsa.

Karanta cikakken babi 2 Tar 13