Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

1 Tar 12:1-22 Littafi Mai Tsarki (HAU)

1. Mutane da yawa suka haɗa kai da Dawuda lokacin da yake a Ziklag, sa'ad da yake a takure saboda Saul ɗan Kish. Su ma suna cikin manyan jarumawan da suka taimake shi yaƙi. Dukansu gwanayen sojoji ne, suna iya su harba kibiya, ko su yi jifa da majajjawa da hannun dama ko da na hagu.

2. Su daga kabilar Biliyaminu ne, dangin Saul.

3-7. Waɗannan su ne shugabannin sojoji,Ahiyezer, da Yowash, 'ya'yan Shemaiya, maza, daga GibeyaYeziyel, da Felet, 'ya'yan Azmawet, mazaBeraka, da Yehu daga AnatotIsmaya daga Gibeyon babban jarumine a cikin jarumawan nan talatin,yana daga cikin shugabanninjarumawa talatin ɗinIrmiya, da YahaziyelYohenan, da Yozabad daga GederaEluzai, da Yerimot, da Be'aliyaShemariya, da Shefatiya daga HarifElkana, da Isshiya, da AzarelYowezer, da Yashobeyam daga iyalinKoraYowela, da Zabadiya 'ya'ya maza naYeroham na Gedor

8. Waɗannan su ne sunayen shahararru, ƙwararrun mayaƙa daga kabilar Gad, waɗanda suka haɗa kai da sojojin Dawuda, sa'ad da yake a kagara a hamada. Su gwanayen yaƙi da garkuwa da mashi ne. Fuskokinsu kamar na zakoki, saurinsu kamar bareyi a kan dutse.

9-13. Ga yadda aka lasafta su bisa ga matsayinsu, da Ezer, da Obadiya, da Eliyab, da Mishmanna, da Irmiya, da Attai, da Eliyel, da Yohenan, da Elzabad, da Irmiya, da Makbannai.

14. Waɗannan daga kabilar Gad shugabannin sojoji ne, waɗansu na mutum dubu, sauransu kuma ƙananan shugabanni ne waɗanda suke shugabancin sojoji ɗari.

15. Su ne waɗanda suka haye Urdun a watan fari na shekara, sa'ad da Kogin Urdun ɗin ya yi ambaliya. Suka kori waɗanda suke zaune a kwaruruka, na wajen gabas da yamma da kogin.

16. Sa'an nan waɗansu daga cikin mazajen Biliyaminu da na Yahuza, suka zo wurin Dawuda a kagararsa.

17. Sai Dawuda ya fito don ya tarye su, ya ce musu, “Idan da salama kuka zo wurina don ku taimake ni, to, zuciyata za ta zama ɗaya da taku, amma idan kun zo ne don ku bashe ni ga maƙiyana, to, Allah na kakanninmu ya duba ya shara'anta, da yake ba ni da laifi.”

18. Ruhun Allah kuwa ya sauko a kan Amasa wanda daga baya ya zama shugaban talatin ɗin, sai ya ce,“Muna tare da kai, ya Dawuda ɗan Yesse!Allah ya ba ka nasara tare da waɗanda suke tare da kai!Allah yana wajenka!”Sa'an nan Dawuda ya marabce su, ya maishe su shugabanni a sojojinsa.

19. Waɗansu sojoji daga Manassa, suka tafi wurin Dawuda sa'ad da yake fita tare da Filistiyawa don su yi yaƙi da Saul. Amma Dawuda bai tafi tare da su ba, domin sarakunan Filistiyawa sun yi shawara, suka sallame shi, don kada ya juya musu gindin baka, ya nemi sulhu a wurin shugabansu Saul, da kawunansu.

20. Sa'ad da yake komawa Ziklag sai sojojin Manassa suka zo wurinsa, wato su Adana, da Yozabad, da Yediyayel, da Maikel, da Yozabad, da Elihu, da Zilletai. A sojojin kabilar Manassa, waɗannan shugabannin sojoji ne na dubu dubu.

21. Suka kuwa taimaki Dawuda sa'ad da mahara take tasar masa, gama dukansu jarumawa ne sosai, su kuma shugabannin sojoji ne.

22. Kowace rana mutane suna ta zuwa wurin Dawuda don su taimake shi, har suka zama babbar runduna.

Karanta cikakken babi 1 Tar 12