Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

1 Sar 2:16-20 Littafi Mai Tsarki (HAU)

16. Yanzu dai ina da roƙo guda zuwa gare ki, kada ki hana mini.”

17. Ta ce masa, “To, sai ka faɗa.”Sai ya ce, “In kin yarda ki yi magana da sarki Sulemanu, gama ba zai ƙi jinki ba, ki ce ya ba ni yarinyar nan, Abishag, daga Shunem, ta zama matata.”

18. Bat-sheba kuwa ta ce, “Da kyau, zan yi wa sarki magana dominka.”

19. Sa'an nan Bat-sheba ta tafi wurin sarki Sulemanu don ta yi magana da shi a kan Adonija. Sarki ya tashi domin ya tarye ta. Ya rusuna mata, sa'an nan ya zauna a kujerar sarautarsa. Ya sa aka kawo mata kujera, ta kuwa zauna a wajen damansa.

20. Sai ta ce, “Ina da wani ɗan roƙo a gare ka, kada ka hana mini shi.”Sarki ya ce mata, “Ya tsohuwata, sai ki faɗi abin da kike so, gama ba zan hana miki ba.”

Karanta cikakken babi 1 Sar 2