Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

1 Sar 17:1-9 Littafi Mai Tsarki (HAU)

1. Wani annabi mai suna Iliya, mutumin Tishbi a Gileyad, ya ce wa sarki Ahab, “Na rantse da Ubangiji, Allah na Isra'ila, wanda nake bauta wa, ba za a yi raɓa ko ruwan sama cikin shekarun nan ba, sai da faɗata.”

2. Sa'an nan Ubangiji ya ce wa Iliya,

3. “Ka tashi daga nan ka nufi wajen gabas, ka ɓuya a rafin Kerit, a gabashin Urdun.

4. Za ka riƙa samun ruwan sha daga rafin, na kuma umarci hankaki su ciyar da kai a can.”

5. Iliya kuwa ya tafi, ya yi yadda Ubangiji ya faɗa, ya tafi ya zauna a rafin Kerit wanda yake gabashin Urdun.

6. Hankaki kuma suka riƙa kawo masa abinci da nama, safe da maraice. Yakan kuma sha ruwa daga rafin.

7. Da aka jima sai rafin ya ƙafe saboda ba a yin ruwan sama a ƙasar.

8. Sa'an nan Ubangiji ya ce wa Iliya.

9. “Tashi ka tafi Zarefat ta Sidon, ka zauna a can. Ga shi, na umarci wata mace wadda mijinta ya rasu ta ciyar da kai.”

Karanta cikakken babi 1 Sar 17