Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

1 Sar 1:47-53 Littafi Mai Tsarki (HAU)

47. Banda wannan kuma, fādawa sun tafi su kai caffa ga sarki Dawuda, suna cewa, ‘Allahnka ya sa Sulemanu ya yi suna fiye da kai, ya kuma fīfita gadon sarautarsa fiye da naka.’ Sai sarki ya sunkuyar da kansa a gadonsa.

48. Sa'an nan ya ce, ‘Yabo ya tabbata ga Ubangiji Allah na Isra'ila wanda ya sa ɗaya daga cikin zuriyata ya hau gadon sarautata yau, idona kuwa ya gani.’ ”

49. Sai baƙin Adonija duka suka tashi suna rawar jiki, kowa ya kama hanyarsa.

50. Adonija kuwa ya ji tsoron Sulemanu, sai ya tashi, ya tafi, ya kama zankayen bagade.

51. Aka faɗa wa Sulemanu cewa ga Adonija yana jin tsoron sarki Sulemanu, gama, ga shi, ya kama zankayen bagade, yana cewa, “Bari sarki Sulemanu ya rantse mini tukuna, cewa ba zai kashe ni ba.”

52. Sulemanu kuwa ya ce, “Idan ya nuna kansa nagarin mutum ne, ko gashin kansa guda ɗaya ba zai faɗi ƙasa ba, amma idan aka iske shi da mugunta, to, lalle kashe shi za a yi.”

53. Sarki Sulemanu kuwa ya aika aka kawo shi daga bagaden. Da ya zo, sai ya rusuna, ya gai da sarki Sulemanu. Sulemanu ya ce masa, “Tafi gidanka.”

Karanta cikakken babi 1 Sar 1