Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

Yah 12:23-38 Littafi Mai Tsarki (HAU)

23. Yesu ya amsa musu ya ce, “Lokaci ya yi da za a ɗaukaka Ɗan Mutum.

24. Lalle hakika, ina gaya muku, in ba an binne ƙwayar alkama ta mutu ba, za ta zauna ita kaɗai. Amma in ta mutu sai ta hayayyafa.

25. Mai ƙaunar ransa zai rasa shi. Wanda kuwa ya ƙi ransa a duniyan nan, ya kiyaye shi ke nan, har ya zuwa rai madawwami.

26. Wanda duk zai bauta mini, ya bi ni. Inda nake kuma, nan bawana zai kasance shi ma. Kowa yake bauta mini, Uba zai girmama shi.”

27. “Yanzu ina jin nauyi a raina. Me zan ce kuwa? In ce, ‘Ya Uba ka ɗauke mini wannan lokaci’? A'a, ai, dā ma na zo ne takanas domin wannan lokaci.

28. Ya Uba, ka ɗaukaka sunanka.” Sai aka ji wata murya daga Sama ta ce, “Na riga na ɗaukaka shi, zan kuma ƙara ɗaukaka shi,”

29. Da taron da yake tsaye a wurin suka ji muryar, suka ce, “An yi cida.” Waɗansu kuwa suka ce, “Wani mala'ika ne ya yi masa magana.”

30. Yesu ya amsa ya ce, “Ba saboda ni aka yi wannan muryan nan ba, sai dominku.

31. Yanzu ne za a yi wa duniyan nan shari'a, yanzu ne kuma za a tuɓe mai mulkin duniyan nan.

32. Ni kuwa bayan an ɗaga ni daga ƙasa zan ja dukan mutane gare ni.”

33. Ta faɗar haka ya kwatanta irin mutuwar da zai yi.

34. Sai taron suka amsa masa suka ce, “Shari'armu ta gaya mana, cewa Almasihu zai tabbata har abada. To, yaya za ka ce lalle ne a ɗaga Ɗan Mutum? Wane ne Ɗan Mutum ɗin?”

35. Yesu ya ce musu, “Haske na tare da ku har ɗan lokaci kaɗan na gaba. Ku yi tafiya tun haske na tare da ku, kada duhu ya ci muku. Mai tafiya a cikin duhu bai san inda yake tafiya ba.

36. Ku gaskata da hasken, tun kuna tare da shi, domin ku zama mutanen haske.”Yesu ya faɗi haka, sa'an nan ya tafi ya ɓuya musu.

37. Amma ko da yake ya sha yin mu'ujizai da yawa a gabansu, duk da haka, ba su gaskata shi ba,

38. domin a cika faɗar Annabi Ishaya cewa,“Ya Ubangiji, wa ya gaskata jawabinmu?Ga wa kuma aka bayyana ikon Ubangiji?”

Karanta cikakken babi Yah 12