Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

W. Yah 1:6-8 Littafi Mai Tsarki (HAU)

6. ya mai da mu firistoci, mallakar Allah Ubansa. Amin.

7. Ga shi, zai zo a cikin gajimare, kowa zai gan shi, har da waɗanda suka soke shi, duk kabilan duniya kuma za su yi kuka a kansa. Wannan haka yake. Amin.

8. “Ni ne Alfa. Ni ne Omega,” in ji Ubangiji Allah, wanda yake a yanzu, shi ne a dā, shi ne kuma a nan gaba, Maɗaukaki.

Karanta cikakken babi W. Yah 1