Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

2 Tas 2:3-6 Littafi Mai Tsarki (HAU)

3. Kada ku yarda kowa yă yaudare ku ko ta halin ƙaƙa, domin wannan rana ba za ta zo ba, sai an yi fanɗarewar nan, sarkin tawaye kuma ya bayyana, wato, hallakakken nan.

4. Shi ne magabci, mai ɗaukaka kansa, yana gāba da duk abin da ya shafi sunan Allah, ko kuma wanda ake yi wa ibada. Har ma yakan zauna a Haikalin Allah, yana cewa, shi ne Allah.

5. Ashe, ba ku tuna ba, nakan gaya muku haka tun muna tare?

6. To, a yanzu dai kun san abin da yake tare shi, don kada ya bayyana kafin lokacinsa.

Karanta cikakken babi 2 Tas 2