Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

2 Kor 6:11-17 Littafi Mai Tsarki (HAU)

11. Ya ku Korantiyawa, ba mu ɓoye muku kome ba, mun saki zuciya da ku ƙwarai.

12. Ai, ba wata rashin yarda a zuciyarmu, sai dai a taku.

13. Ina roƙonku kamar 'ya'yana, ku ma ku saki zuciya da mu.

14. Kada ku yi cuɗanya marar dacewa da marasa ba da gaskiya. To, me ya haɗa aikin adalci da na mugunta? Ko kuwa me ya haɗa haske da duhu?

15. Ina kuma jiyayyar Almasihu da iblis? Me kuma ya haɗa mai ba da gaskiya da marar ba da gaskiya?

16. Wace yarjejeniya ce take a tsakanin Haikalin Allah da gumaka? Domin mu haikali ne na Allah Rayayye. Yadda Allah ya ce,“Zan zauna tare da su, in yi yawo a tsakaninsu,Zan kuma kasance Allahnsu,Su kuma su kasance jama'ata.

17. Saboda haka, sai ku fito daga cikinsu,Ku keɓe, in ji Ubangiji,Kada ku ko taɓa wani abu marar tsarki,Ni kuwa in yi na'am da ku,

Karanta cikakken babi 2 Kor 6