Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

1 Yah 3:10-13 Littafi Mai Tsarki (HAU)

10. Ta haka sai a ga waɗanda suke 'ya'yan Allah, da kuma waɗanda suke 'ya'yan Iblis, wato duk wanda ba ya aikata adalci, ba na Allah ba ne, haka kuma wanda ba ya ƙaunar ɗan'uwansa.

11. Wannan shi ne jawabin da kuka ji tun farko, cewa dai mu ƙaunaci juna,

12. kada mu zama kamar Kayinu, wanda yake na Mugun, har ma ya kashe ɗan'uwansa. To, don me ya kashe shi? Don ayyukansa mugaye ne, na ɗan'uwansa kuwa na kirki ne.

13. Kada ku yi mamaki, 'yan'uwa, idan duniya take ƙinku.

Karanta cikakken babi 1 Yah 3