Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

Zak 7:4-7 Littafi Mai Tsarki (HAU)

4. Sa'an nan Ubangiji Mai Runduna ya yi mini magana, ya ce,

5. in faɗa wa dukan mutanen ƙasar da firistoci, in ce, “Sa'ad da kuka yi azumi da baƙin ciki a watan biyar da na bakwai dukan shekarun nan saba'in, saboda ni ne kuka yi azumin?

6. Sa'ad da kuma kuke ci, kuna sha, ba don kanku ne kuke ci, kuke sha ba?”

7. Maganar ke nan da Ubangiji ya faɗa ta bakin annabawan dā, a lokacin akwai mutane da arziki cikin Urushalima da garuruwa kewaye da ita, a lokacin kuma akwai mutane a Negeb da gindin tuddai.

Karanta cikakken babi Zak 7