Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

Zak 7:2-6 Littafi Mai Tsarki (HAU)

2. Sai mutanen Betel suka aiki Sharezer da Regem-melek da mutanensu su nemi tagomashi a wurin Ubangiji,

3. su kuma tambayi firistocin Haikalin Ubangiji da annabawa, cewa ko ya kamata su yi baƙin ciki da azumi a watan biyar kamar yadda suka saba yi a shekarun baya?

4. Sa'an nan Ubangiji Mai Runduna ya yi mini magana, ya ce,

5. in faɗa wa dukan mutanen ƙasar da firistoci, in ce, “Sa'ad da kuka yi azumi da baƙin ciki a watan biyar da na bakwai dukan shekarun nan saba'in, saboda ni ne kuka yi azumin?

6. Sa'ad da kuma kuke ci, kuna sha, ba don kanku ne kuke ci, kuke sha ba?”

Karanta cikakken babi Zak 7