Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

Zak 11:1-6 Littafi Mai Tsarki (HAU)

1. Ki buɗe ƙofofinki, ke Lebanon,Don wuta ta cinye itatuwan al'ul naki.

2. Ka yi kuka, kai itacen kasharina,Gama itacen al'ul ya riga ya fāɗi,Itatuwa masu daraja sun lalace,Ku yi kuka, ku itatuwan oak na Bashan,Saboda an sassare itatuwan babban kurmi.

3. Ku ji kukan makiyaya,Gama an ɓata musu darajarsu.Ji rurin zakoki,Gama an lalatar da jejin Urdun.

4. Ga abin da Ubangiji Allah ya faɗa, “Ka zama makiyayin garken tumakin da za a yanka.

5. Masu sayensu za su yanyanka su, ba za a kuwa hukunta su ba. Masu sayar da su kuma za su yi hamdala gare ni, su ce sun sami dukiya. Makiyayansu kuwa ba su ji tausayinsu ba.

6. “Gama ba zan ƙara jin tausayin mazaunan ƙasan nan ba, ni Ubangiji na faɗa. Ga shi, zan sa su fāɗa a hannun junansu da a hannun sarkinsu. Za su lalatar da ƙasar, ba kuwa zan cece su daga hannunsu ba.”

Karanta cikakken babi Zak 11