Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

Zab 9:6-16 Littafi Mai Tsarki (HAU)

6. An hallaka abokan gābanmu har abada,Ka lalatar da biranensu,An kuma manta da su sarai.

7. Amma Ubangiji sarki ne har abada,Ya kafa kursiyinsa domin yin shari'a.

8. Yana mulkin duniya da adalci,Yana yi wa mutane shari'a da gaskiya.

9. Ubangiji mafaka ne ga waɗanda ake zalunta,Wurin ɓuya a lokatan wahala.

10. Waɗanda suka san ka za su amince da kai, ya Ubangiji,Ba za ka ƙyale duk wanda ya zo gare ka ba.

11. Ku yabi Ubangiji, shi da yake mulki a Sihiyona!Ku faɗa wa kowace al'umma abin da ya yi!

12. Allah yana tunawa da waɗanda suke shan wuya,Ba ya mantawa da kukansu,Yana kuma hukunta waɗanda suke cutarsu.

13. Ya Ubangiji, ka yi mini jinƙai!Ka dubi irin wulakancin da maƙiya suka yi mini!Ka kuɓutar da ni daga mutuwa, ya Ubangiji,

14. Domin in iya tsayawa a gaban jama'ar Urushalima,In faɗa musu dukan abin da ya sa nake yabonka.Zan yi farin ciki saboda ka cece ni.

15. Arna sun haƙa rami sun kuwa fāɗa ciki,Sun ɗana tarko, ya kuwa kama su.

16. Ubangiji ya bayyana kansa ta wurin shari'arsa mai adalci,Mugaye sun kama kansu da abubuwan da suka aikata.

Karanta cikakken babi Zab 9