Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

Zab 76:6-12 Littafi Mai Tsarki (HAU)

6. Sa'ad da ka fafare su, ya Allah na Yakubu,Dawakansu da mahayansu suka fāɗi matattu.

7. Amma mutane suna jin tsoronka!Wa zai iya tsayawa a gabankaSa'ad da ka yi fushi?

8. Daga Sama ka sanar da shari'arka,Duniya ta tsorata, ta yi tsit,

9. Sa'ad da ka tashi domin ka yanke hukunci,Domin ka ceci waɗanda ake zalunta a duniya.

10. Hasalar mutane ba ta ƙara kome, sai dai ta ƙara maka yabo.Waɗanda suka tsira daga yaƙe-yaƙe za su kiyaye idodinka.

11. Ku ba Ubangiji Allahnku abin da kuka alkawarta masa,Dukanku sauran al'umma da kuke kusa, ku kawo masa kyautai.Allah yakan sa mutane su ji tsoronsa,

12. Yakan ƙasƙantar da shugabanni masu girmankai,Ya tsoratar da manyan sarakuna.

Karanta cikakken babi Zab 76