Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

Zab 75:3-10 Littafi Mai Tsarki (HAU)

3. Ko da duniya da dukan waɗanda yake zaune cikinta za su ɓace,Zan ƙarfafa harsashin gininta.

4. Na faɗa wa masu girmankai kada su yi taƙama,Na kuma faɗa wa mugaye kada su yi fāriya,

5. Na dai faɗa musu su daina yanga,Su daina yin taƙama.”

6. Hukunci ba daga gabas, ko yamma,Ko daga kudu, ko arewa yake zuwa ba.

7. Allah yake yin shari'a,Yana ƙasƙantar da waɗansu, ya kuma ɗaukaka waɗansu.

8. Ubangiji yana riƙe da ƙoƙo,Cike da sabon ruwan inabi mai ƙarfi,Yana zuba shi, dukan mugaye kuwa suna ta sha,Suka shanye shi ƙaƙaf.

9. Amma har abada ba zan daina yin magana a kan Allah na Yakubu ba,Ko in daina raira yabbai gare shi.

10. Shi zai karya ikon mugaye,Amma za a ƙara wa masu adalci ƙarfi.

Karanta cikakken babi Zab 75