Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

Zab 32:7-11 Littafi Mai Tsarki (HAU)

7. Kai ne maɓoyata,Za ka cece ni daga wahala.Ina raira waƙa da ƙarfi saboda cetonka,Domin ka kiyaye ni.

8. Ubangiji ya ce, “Zan koya maka hanyar da za ka bi,Zan koya maka, in kuma ba ka shawara.

9. Kada ka zama wawa kamar doki ko alfadari,Wanda dole sai da linzami, da ragama za a sarrafa shi,Sa'an nan yă yi maka biyayya.”

10. Tilas ne mugu yă sha wahala,Amma masu dogara ga Ubangiji,Madawwamiyar ƙaunarsa tana kiyaye su.

11. Dukanku adalai, ku yi murna,Ku yi farin ciki,Saboda abin da Ubangiji ya yi!Dukanku da kuke yi masa biyayya,Ku yi sowa ta farin ciki!

Karanta cikakken babi Zab 32