Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

Yush 10:10-14 Littafi Mai Tsarki (HAU)

10. Zan fāɗa wa waɗannan mutane masu zunubi, in hukunta su.Za a tattara al'ummai, su yi gāba da su,Za a hukunta su saboda yawan zunubansu.

11. “Ifraimu horarriyar karsana ce,Wadda yake jin daɗin yin sussuka,Amma na sa wa kyakkyawan wuyanta karkiya,Na sa Yahuza ta ja garmar noma,Yakubu kuwa za ta ja garmar bajiya.

12. Ku shuka wa kanku adalci,Ku girbe albarkun ƙauna,Ku yi kautun saurukanku,Gama lokacin neman Ubangiji ya yi,Domin ya zo, ya koya muku adalci.

13. Kun shuka mugunta,Kun girbe rashin adalci,Kun ci amfanin ƙarya.“Da yake dogara ga hanyarku da ɗumbun sojojinku,

14. Domin haka hayaniyar yaƙi za ta tashi a tsakanin jama'arku.Dukan kagaranku za a hallaka su.Kamar yadda Shalmanesar ya hallaka Bet-arbel a ranar yaƙi.An fyaɗa uwaye da 'ya'yansu a ƙasa.

Karanta cikakken babi Yush 10