Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

Yow 2:6-21 Littafi Mai Tsarki (HAU)

6. Da zuwanta mutane sukan firgita,Dukan fuskoki sukan ɓaci.

7. Takan auka kamar mayaƙa,Takan hau garu kamar sojoji,Takan yi tafiya,Kowa ta miƙe sosai inda ta sagaba,Ba ta kaucewa.

8. Ba ta hawan hanyar juna,Kowa tana bin hanyarta.Takan kutsa cikin abokan gāba, ba aiya tsai da ita.

9. Takan ruga cikin birni,Takan hau garu a guje,Takan hau gidaje,Takan shiga ta tagogi kamar ɓarawo.

10. Duniya takan girgiza saboda ita,Sammai sukan yi rawar jiki.Rana da wata sukan duhunta,Taurari kuwa sukan dainahaskakawa.

11. Ubangiji yakan umarci rundunarsa,Rundunarsa mai cika umarninsababba ce, mai ƙarfi,Gama ranar Ubangiji babba ce maibanrazana.Wa zai iya daurewa da ita?

12. “Koyanzu,” in ji Ubangiji,“Ku juyo wurina da zuciya ɗaya,Da azumi, da kuka, da makoki,

13. Ku kyakkece zuciyarku, ba tufafinkukaɗai ba.”Ku komo wurin Ubangiji Allahnku.Gama shi mai alheri ne, mai jinƙai,Mai jinkirin fushi ne, mai yawanƙauna,Yakan tsai da hukunci.

14. Wa ya sani ko Ubangiji Allahnmu zaisāke nufinsa,Ya sa mana albarka,Har mu miƙa masa hadaya ta gari data sha?

15. Ku busa ƙaho a Sihiyona,Ku sa a yi azumi,Ku kira muhimmin taro.

16. Ku tattara jama'a wuri ɗaya,Ku tsarkake taron jama'a,Ku tattara dattawa da yara,Har da jarirai masu shan mama.Ku sa ango ya fito daga cikinturakarsa,Amarya kuma ta fito daga cikinɗakinta.

17. Sai firistoci masu hidimar Ubangiji,Su yi kuka a tsakanin shirayi dabagade,Su ce, “Ya Ubangiji, ka cecijama'arka,Kada ka bar gādonka ya zama abinzargiDa abin ba'a a tsakiyar al'ummai.Don kada al'ummai su ce,‘Ina Allahnsu?’ ”

18. Sai Ubangiji ya ji kishin ƙasarsa,Ya kuma ji ƙan mutanensa.

19. Sa'an nan ya ce musu,“Ga shi, zan ba ku hatsi da ruwaninabi, da mai,Za ku ƙoshi.Ba zan sa ku ƙara zama abin zargi gaal'ummai ba.

20. Zan kawar muku da waɗanda sukazo daga arewa,Zan kori waɗansunsu zuwa cikinhamada.Zan kori sahunsu na gaba zuwa cikinTekun Gishiri,Zan kori sahunsu na baya, zuwacikin Bahar Rum.Gawawwakinsu za su yi ɗoyi.Zan yi musu haka saboda dukan abinda suka yi muku.”

21. Kada ki ji tsoro, ya ƙasa,Ki yi farin ciki, ki yi murna,Gama Ubangiji ne ya yi waɗannanmanyan al'amura.

Karanta cikakken babi Yow 2