Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

Yow 2:12-31 Littafi Mai Tsarki (HAU)

12. “Koyanzu,” in ji Ubangiji,“Ku juyo wurina da zuciya ɗaya,Da azumi, da kuka, da makoki,

13. Ku kyakkece zuciyarku, ba tufafinkukaɗai ba.”Ku komo wurin Ubangiji Allahnku.Gama shi mai alheri ne, mai jinƙai,Mai jinkirin fushi ne, mai yawanƙauna,Yakan tsai da hukunci.

14. Wa ya sani ko Ubangiji Allahnmu zaisāke nufinsa,Ya sa mana albarka,Har mu miƙa masa hadaya ta gari data sha?

15. Ku busa ƙaho a Sihiyona,Ku sa a yi azumi,Ku kira muhimmin taro.

16. Ku tattara jama'a wuri ɗaya,Ku tsarkake taron jama'a,Ku tattara dattawa da yara,Har da jarirai masu shan mama.Ku sa ango ya fito daga cikinturakarsa,Amarya kuma ta fito daga cikinɗakinta.

17. Sai firistoci masu hidimar Ubangiji,Su yi kuka a tsakanin shirayi dabagade,Su ce, “Ya Ubangiji, ka cecijama'arka,Kada ka bar gādonka ya zama abinzargiDa abin ba'a a tsakiyar al'ummai.Don kada al'ummai su ce,‘Ina Allahnsu?’ ”

18. Sai Ubangiji ya ji kishin ƙasarsa,Ya kuma ji ƙan mutanensa.

19. Sa'an nan ya ce musu,“Ga shi, zan ba ku hatsi da ruwaninabi, da mai,Za ku ƙoshi.Ba zan sa ku ƙara zama abin zargi gaal'ummai ba.

20. Zan kawar muku da waɗanda sukazo daga arewa,Zan kori waɗansunsu zuwa cikinhamada.Zan kori sahunsu na gaba zuwa cikinTekun Gishiri,Zan kori sahunsu na baya, zuwacikin Bahar Rum.Gawawwakinsu za su yi ɗoyi.Zan yi musu haka saboda dukan abinda suka yi muku.”

21. Kada ki ji tsoro, ya ƙasa,Ki yi farin ciki, ki yi murna,Gama Ubangiji ne ya yi waɗannanmanyan al'amura.

22. Kada ku ji tsoro, ku dabbobinsaura,Gama wuraren kiwo a jeji sun yi koreshar.Itatuwa suna ta yin 'ya'ya,Itacen ɓaure da kurangar inabi sunata yin 'ya'ya sosai.

23. Ya ku mutanen Sihiyona, ku yimurna,Ku yi farin ciki da UbangijiAllahnku,Gama ya ba ku ruwan farkoDomin shaidar gafarar da ya yimuku,Ya kwararo muku da ruwan farko dana ƙarshe da yawa kamar dā.

24. Masussukai za su cika da hatsi,Wuraren matse ruwan inabi za sumalala da ruwan inabi.

25. “Zan mayar muku da abin da kukayi hasararsaA shekarun da fara ta cinyeamfaninku,Wato ɗango da fara mai gaigayewa,da mai cinyewa,Su ne babbar rundunata wadda naaiko muku.

26. Yanzu za ku ci abinci a wadace kuƙoshi,Za ku yabi sunan UbangijiAllahnku,Wanda ya yi muku abubuwa masubanmamaki,Ba kuma za a ƙara kunyatar damutanena ba.

27. Ku mutanen Isra'ila, za ku sani inacikinku,Ni ne kuwa Ubangiji Allahnku, bawani kuma,Ba kuma za a ƙara kunyatar damutanena ba.”

28. “Bayan wannan zan zubo Ruhuna akan jama'a duka,'Ya'yanku mata da maza za su iyarda saƙona,Tsofaffinku kuwa za su yi mafarkai,Samarinku za su ga wahayi da yawa.

29. A lokacin zan zubo Ruhuna,Har a kan barori mata da maza.

30. “Zan yi faɗakarwa a kan wannanranaA sararin sama da a duniya.Za a ga jini, da wuta, da murtukewarhayaƙi,

31. Rana za ta duhunta,Wata zai zama ja wur kamar jini,Kafin isowar babbar ranan nan maibantsoro ta Ubangiji.

Karanta cikakken babi Yow 2