1. Annabcin Obadiya ke nan.Wannan shi ne abin da Ubangiji Allah ya ce a kan al'ummar Edom.Ubangiji ya aiki manzonsa wurinsauran al'umma,Mun kuwa ji saƙonsa cewa,“Ku zo! Mu tafi mu yi yaƙi daEdom!”
2. Ubangiji ya ce wa al'ummar Edom,“Zan maishe ki ƙanƙanuwa a cikinsauran al'umma,Za a raina ki ƙwarai.
3. Girmankanki ya yaudare ki,Kina zaune a kagara, a kan dutse,Wurin zamanki yana canƙwanƙolin duwatsu.Don haka a zuciya kike cewa,‘Wa zai saukar da ni ƙasa?’
4. Ko da yake kina shawagi can samakamar gaggafa,Gidanki kuma yana can cikin taurari,Daga can zan saukar da ke,” in jiUbangiji