Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

Mak 2:14-21 Littafi Mai Tsarki (HAU)

14. Annabawanki sun gano miki wahayan ƙarya,Ba su tone asirin muguntarki,Har da za a komo da ke daga bauta ba.Amma suka yi miki annabcin ƙarya na banza.

15. Dukan masu wucewa suna yin miki tafin raini.Suna yi wa Urushalima tsāki,Suna kaɗa mata kai, suna cewa,“Ai, Urushalima ke nan,Birnin nan da ake cewa mai cikakken jamali,Wanda ya ƙayatar da dukan duniya?”

16. Maƙiyanki duka sun wage bakinsu gāba da ke,Suna tsāki, suna cizon bakinsu,Suna ihu, suna cewa, “Mun hallaka ta!Ai, wannan ita ce ranar da muke fata!Ga shi kuwa, ta zo, mun gan ta!”

17. Ubangiji ya aikata abin da ya yi niyya,Ya cika maganarsa wadda ya faɗa tun dā,Ya hallakar, ba tausayi,Ya sa maƙiyi ya yi murna a kanki,Ya ƙarfafa ƙarfin maƙiyanki.

18. Ya Sihiyona, ki yi kuka ga Ubangiji,Bari hawayenki su gudana dare da rana kamar ruwan rafi,Kada ki huta, kada kuma idanunki su huta!

19. Ki tashi, ki ya ta kuka dukan dare,Ki bulbule abin da yake cikin zuciyarkiKamar ruwa gaban Ubangiji.Ki miƙa hannuwanki zuwa gare shi,Saboda rayukan 'ya'yanki,Waɗanda suke suma da yunwaA magamin kowane titi!

20. Ya Ubangiji, ka duba, ka gani!Wane ne ka yi wa haka?Mata za su cinye 'ya'yansu da suke reno?Ko kuwa za a kashe firist da annabiA cikin Haikalin Ubangiji?

21. Yara da tsofaffi suna kwance cikin ƙurar tituna,An kashe 'ya'yana, 'yan mata da samari, da takobi.Ka kashe su a ranar fushinka, ba tausayi.

Karanta cikakken babi Mak 2