Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

M. Sh 31:1-5 Littafi Mai Tsarki (HAU)

1. Sai Musa ya ci gaba da yi wa dukan Isra'ilawa magana.

2. Ya ce, “Yau shekarata ɗari da ashirin ne, ba na iya kaiwa da komowa. Ubangiji kuwa ya ce mini, ‘Ba za ka haye wannan Urdun ba.’

3. Ubangiji Allahnku shi ne zai yi gaba ya haye, ya hallaka al'umman da take gabanku don ku ci su. Joshuwa ne zai shugabance ku, ya haye kamar yadda Ubangiji ya faɗa.

4. Ubangiji zai yi musu kamar yadda ya yi wa Sihon da Og, sarakunan Amoriyawa, da ƙasarsu, sa'ad da ya hallaka su.

5. Ubangiji zai bashe su a gare ku. Za ku yi musu kamar yadda dā na umarce ku.

Karanta cikakken babi M. Sh 31