Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

L. Mah 8:20-28 Littafi Mai Tsarki (HAU)

20. Ya ce wa Yeter, ɗan farinsa, “Tashi, ka kashe su.” Amma saurayin bai zare takobinsa ba, gama yana jin tsoro domin shi yaro ne.

21. Sai Zeba da Zalmunna suka ce, “Tashi da kanka, ka kashe mu, gama yadda mutum yake haka kuma ƙarfinsa yake.” Gidiyon kuwa ya tashi ya kashe Zeba da Zalmunna. Ya kwance kayan ado daga wuyan raƙumansu.

22. Sa'an nan mutanen Isra'ila suka ce wa Gidiyon, “Ka yi mulkinmu, kai da 'ya'yanka, da jikokinka, gama ka cece mu daga hannun Madayanawa.”

23. Gidiyon ya ce musu, “Ba zan yi mulkinku ba, ɗana kuma ba zai yi mulkinku ba, Ubangiji ne zai yi mulkinku.”

24. Ya ci gaba ya ce, “Ina roƙon kowannenku ya ba ni 'yan kunne daga cikin ganimar da ya kwaso.” (Gama Madayanawa suna da 'yan kunne na zinariya, gama su mutanen hamada ne.)

25. Suka ce, “Lalle, za mu ba ka su.” Nan da nan suka shimfiɗa mayafi, kowa ya zuba 'yan kunnen da ya kwaso ganima.

26. Nauyin 'yan kunnen zinariya da ya roƙa ya kai shekel dubu ɗaya da ɗari bakwai (1,700), banda kayan ado, da na rataye-rataye, da tufafin shunayya waɗanda sarakunan Madayanawa suke sawa, banda ɗan gaba da yake a wuyan raƙumansu.

27. Gidiyon kuwa ya yi gunki da zinariyar, ya ajiye a birninsa, wato Ofra. Isra'ilawa kuma suka bar bin Allah, suka tafi can domin su yi wa gunkin sujada, ya zama tarko ga Gidiyon da iyalinsa.

28. Da haka Isra'ilawa suka mallaki Madayanawa har ba su zamar musu barazana ba. Ƙasar kuwa ta zauna lafiya shekara arba'in a zamanin Gidiyon.

Karanta cikakken babi L. Mah 8