Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

L. Mah 20:15-20 Littafi Mai Tsarki (HAU)

15. A ran nan mutanen Biliyaminu suka tattaru daga garuruwansu, mutum dubu ashirin da shida (26,000). Banda waɗannan, sai da mazaunan Gibeya suka tara zaɓaɓɓun mutane ɗari bakwai.

16. Daga cikin waɗannan duka akwai zaɓaɓɓun mutane bakwai, bahagwai. Kowannensu yana iya ya baraci gashi guda da majajjawa ba kuskure.

17. Isra'ilawa kuwa banda kabilar Biliyaminu, suka tara mayaƙa dubu ɗari huɗu (400,000) horarru.

18. Isra'ilawa suka tashi suka tafi Betel. A can suka yi tambaya ga Allah suka ce, “Wace kabila ce daga cikinmu za ta fara faɗa wa kabilar Biliyaminu?”Ubangiji ya ce, “Kabilar Yahuza ce za ta fara.”

19. Sa'an nan Isra'ilawa suka tashi da safe suka kafa sansani kusa da Gibeya.

20. Suka kuwa fita su yi yaƙi da mutanen Biliyaminu, suka jā dāgar yaƙi suna fuskantar Gibeya.

Karanta cikakken babi L. Mah 20