Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

L. Mah 14:13-17 Littafi Mai Tsarki (HAU)

13. Amma idan kun kāsa ba ni amsar, to, ku ne za ku ba ni rigunan lilin talatin da waɗansu rigunan na ado.”Sai suka ce, “To, faɗi ka-cici-ka-cicin mu ji.”

14. Sai ya ce musu,“Daga mai ci, abinci ya fito,Daga kuma mai ƙarfi, zaƙi ya fito.”Ba su iya ba da amsar ba har kwana uku.

15. A rana ta huɗu suka ce wa matar Samson, “Ki rarrashi mijinki ya gaya mana amsar ka-cici-ka-cicin, idan kuwa kin ƙi, to, za mu ƙone ki da gidan mahaifinki da wuta. Kun gayyace mu don ku tsiyata mu ne?”

16. Sai matar Samson ta yi kuka a gabansa tana cewa, “Kai dai maƙiyina ne, ba masoyina ba, ka yi wa mutanena ka-cici-ka-cici, amma ba ka gaya mini amsarsa ba.”Amma ya ce mata, “Ko iyayena ma ban faɗa musu ba, sai in faɗa miki?”

17. Ta kuwa yi ta yi masa kuka har rana ta bakwai ta ƙarewar bikinsu. Amma a rana ta bakwai, ya faɗa mata amsar saboda yawan fitinarta. Ita kuwa ta faɗa wa mutanenta amsar ka-cici-ka-cicin.

Karanta cikakken babi L. Mah 14